Latest posts

Search found 3 matches:


admin
Admin

44, male

Posts: 3

Re: FA'IDODIN GANYAN MANGWARO

from admin on 11/10/2017 05:04 AM

Allah ka sa mudace

Reply

admin
Admin

44, male

Posts: 3

FA'IDODIN GANYAN MANGWARO

from admin on 11/10/2017 05:00 AM

*FA'IDODIN GANYEN MANGWARO,MUSAMMAN WAJEN MAGANIN CIWON SUGA DA HAWAN JINI DA SAURANSU*: .....Balarabe Shehu Illelah, kasar Sin (China)..... Ko kun san cewa masana ilimin kimiyyar magunguna, na kasar Sin da India, sun tabbatar da cewar daya daga cikin manyan magungunan warkar da ciwon suga (diabetes) shine *Ganyen Mangwaro*? *Ganyen Mangwaro* na dauke da sinadarai masu yawan gaske da ke amfana wa jikin Dan’adam, amma kash, mutane da dama basu san hakan ba ! Yadda ake amfani da shi a matsayin *Maganin cutar ciwon Suga* ( Diabetes) (1) A tsinko ganyan Mangwaro,masu kyau. A wanke su sosai (2) A sanya ruwa a murhu, a tafasashi, har na tsawon minti biyar ba tare da ganyen ba. (3) Sai a zuba ganyen a cikin ruwan zafin da ke kan murhu,tare da OLIVE Oil (wato Man Zaitun). A barshi yayi ta tafasa, har na tsawon mintuna biyar zuwa goma. (4) Sai a sauke shi a tace. (5) Sai a sanya shi cikin kwano ko gilashi mai kyau, a barshi ya kwana (6) Sai a sha wannan ruwan da sassafe bayan an tashi daga barci, kafin ka ci komai. Wannan maganin, yana kawar da abubuwa (marasa kyau masu guba) daga jikin mutum, kuma yana rage yawan suga da ke cikin jini. Haka kuma yana saukar da hawan jini sosai. *ASTHMA,TARI, KO MATSALAR NUMFASHI* yakan sa a samu numfashi mai kyau,kuma cikin sauki,da yardar Allah. *YAWAN FARGABA, ZAMAN DAR-DAR KO RASHIN NUTSUWA* (restlessness): Idan aka zuba cokali biyu zuwa uku, a cikin ruwan wanka, sannan ayi wanka dashi. Yana sanya aji jiki garau, kuma aji hankali ya kwanta,da yardar Allah. *DUTSEN DAKE ZAMA CIKIN HANTA,MADATA KO KODA* (wato *kidney stone*). Mai wannan ciwon, zai busar da ganyen Mangwaro (a inuwa), sannan ya daka shi. A zuba garin a cikin kofi/glass ko kwano, a barshi ya kwana. A rinka sha kullum da safe. Wannan yana narkar da dutsen dake jikin koda sosai,da yardar Allah (swt). *CIWON TARI,GUSHEWAR MURYA KO ASTHMA* A dafa ganyen Mangwaro, a sanya masa Zuma (kadan). Yana taimakawa kwarai da gaske cikin sauri. *CIWON ATINI,KO KASHIN JINI* Sai a shanya ganyen a inuwa a busar dashi a kuma mayar dashi gari, a rinka sha sau uku a rana . Yana tsayar da cutar atini. *CIWON KUNNE* Idan aka tatse ruwan ganyen Mangwaro aka dan dafa shi, sai a rinka digawa a cikin kunnen. Wannan yana *maganin ciwon kunne*. *KUNAR WUTA* Sai a kona ganyen Mangwaro har ya zama toka. Sai kuma a rinka barbadawa a wurin da aka kone. Yana warkar da kunar cikin sauri. Zai kuma bushe da gaggawa In Sha-Allahu. *YAWAN SHAQUWA DA CIWON MAKOGORO* Idan ana shakuwa ko zafin makogwaro,sai a kona ganyen Mangwaro a shaki hayakin. Yana *tsayar da shakuwan da ciwon makogwaro*. *CIWON CIKI* Idan ana yawan *Ciwon Ciki* sai a sanya ganyen Mangwaro a cikin ruwan dumi, a barshi ya kwana, sannan a sha da safe kafin aci komai. In an juri yin hakan yana warkar da *Ciwon Ciki* kowane iri ne,in Allah Ya yarda. *Shan ganyen mangwaro a kai a kai yana kuma kara inganta garkuwan jiki kuma yana maganin hana kumburin ciki*. Yana da kyau ka jurewa shan ganyen Mangwaro a duk safiya, domin ganin yadda suga dake cikin jikin ka, zai sauka cikin sauri in Allah (SWT) Ya yarda.

Reply

admin
Admin

44, male

Posts: 3

Shin suwane zasu zauna A inuwar Alarshi

from admin on 11/07/2017 01:59 PM

WADANDA ZASU ZAUNA KARKASHIN INUWAR AL'ARSHI : TAMBAYA TA 2395 ******************** Assalamu alaykum Allah ya kara muku lafiya ya baku ladan taimakonmu da kukeyi, pls inada question and it's kind of urgent Allah yasa ku samu damar amsa min. Dan Allah hadith guda 1 nake son ku fada min wanda aka irgo wanda zasu shiga karkashin al'arshin Allah ranar alkiyama (banda hadith din da yake cikin bughyatu kulli Muslim). Jazakumullah AMSA ******* Wa alaikis salam wa rahmatullahi wa barakatuhu. Shi wancan Mashahurin hadithin da kike fada, ina jin shine wanda Imamul Bukhariy da Muslim da Nisa'iy da Tirmidhiy da Imamu Malik suka ruwaitoshi ta hanyar Sayyiduna Abu Hurairah. To bayan Abu Hurairah din an ruwaito irinsa ta wajen Sahabbai da dama kamar : - Abu Sa'eed Alkhudriy. - Salmanul Farisiy. - Abud Darda'i. - Mu'az bn Jabal. - Al'irbaadh bn Sariyah. (Yardar Allah ta tabbata garesu baki daya). To bayan shi akwai wani hadisin Sahihi wanda aka ruwaito daga wani Sahabi mai suna Abul Yusri (ra) yace "Naji Manzon Allah (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) yana cewa : "DUK WANDA YA JINKIRTA MA WANDA YAKE CIKIN TSANANI KO KUMA YA SAUKE MASA (BASHIN DA AKE BINSA KENAN). TO ALLAH ZAI INUWANTAR DASHI ARANAR DA BABU WATA INUWA SAI TASA". Abdu bn Humayd da Imamu Ahmad sun ruwaitoshi acikin Musnadansu. Imamu Muslim ma ya kawo wani hadisin mai irin Ma'anarsa acikin wata Qissah. Haka ma Ibnu Maajah. Imamud Daramiy ya ruwaito wani hadisin SAHIHI acikin Musnadu nasa ta hanyar Abu Qataadah (ra) yace Naji Manzon Allah (saww) yana cewa : "DUK WANDA YA JINKIRTA MA WANDA YAKE BI BASHI, KO KUMA YA SHAFE MASA BASHIN, TO ZAI ZAMANTO ACIKIN INUWAR AL'ARSHI ARANAR ALQIYAMAH". Ga wani ma daga Sayyiduna Anas bn Malik (rta) daga Manzon Allah (saww) yana cewa : "MUTUM UKU SUNA CIKIN INUWAR AL'ARSHIN ALLAH ARANAR DA BABU WATA INUWA SAI DAI TASHI : - WANDA YA YAYE DAMUWAR WANI MAI DAMUWA DAGA AL'UMMATA. - WANDA YA RAYA SUNNAH TA. - DA KUMA WANDA YA YAWAITA SALATI AGARENI". Daylamiy ne ya ruwaitoshi. To ga guda uku nan domin Qarin fa'idah. Idan kuma ana buqatar wasu, aduba littafin Imamus Suyutiy mai suna "BUZUGUL HILAAL". WALLAHU A'ALAM. DAGA ZAUREN FIQHU (07-11-2017 18-0

Reply

« Back to previous page